7 Yuni 2026 - 07:35
Source: ABNA24
Isra'ila Na Ƙara Shiga Tsaka Mai Wuya A Lebanon

Halin da Isra'ila ke ciki a Lebanon a yanzu ya fi na watanni uku da suka gabata muni.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) (ABNA): Nir Dvori, manazarcin soji na gidan talabijin din Isra'ila Channel-12, ya ce saboda rikicin da ke ci gaba da faruwa, Tel Aviv na rasa abin da ta samu sannu a hankali, kuma ba za ta iya kiyaye matsayinta da ta samu a baya a fagen Lebanon ba.

Manazarcin soji na yahudawa ya ce: A lokacin da sojojin Isra'ila ke aiki a yankin Blue Line da arewacin kogin Litani, Hizbullah ta gano wata tankar Isra'ila ta kai mata hari da makami mai linzami mai lalata tankuna. Sakamakon haka, kwamandan tankar ya mutu.

A cewar Dvori, muhimmin canji a cikin 'yan makonnin da suka gabata shi ne raguwar tasirin karfin Amurka. Ya ce, ko da shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana wani matsayi, bangarorin Tehran da Beirut ba sa ɗaukarsa da muhimmanci kamar da, wanda hakan ci gaba ne mara kyau ga Isra'ila.

Ya kara da cewa, a da, sojojin Isra'ila suna da 'yanci da yawa wajen gudanar da hare-hare a Lebanon da kai hari kan manufa daban-daban, amma a yanzu wannan damar ta ragu sosai.

Dvori ya yi iƙirarin cewa, Hizbullah na ƙara ƙarfafa ƙarfinsu kuma suna gudanar da ayyuka da ƙarin ƙarfin gwiwa. Sakamakon haka, babban sakataren ƙungiyar, Naim Qassem, yana iya fito fili ya yi adawa da sharuɗɗan Amurka.

………………………………………

Your Comment

You are replying to: .
captcha